NSCDC Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Satar Ƙarafunan Layin Dogo A Kano



Rundunar tsaro ta NSCDC a jihar Kano ta kama wani matashi mai shekara 22 da ake zargi da lalata kayayyakin layin dogo na aikin jirgin ƙasa na gwamnatin tarayya tsakanin Kaduna da Kano.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, SC Ibrahim Idris Abdullahi, ya fitar, ya ce an kama wanda ake zargin mai suna Sani Ismail ne a ƙaramar hukumar Kiru bayan samun bayanan sirri.

Sanarwar ta ce bincike ya nuna cewa matashin ya cire wasu sassan layin dogo guda 11 daga sabon aikin layin dogo da ake ginawa.

Rundunar ta kuma ce an same shi da guduma da ake zargin ya yi amfani da ita wajen aikata laifin.

Haka kuma, NSCDC ta kama wasu mutane biyu, Yusuf Usman da Muhd Auwal, bisa zargin yin sojan gona a matsayin jami’an rundunar duk da cewa ba su cikin rajistar masu aikin sa kai na NSCDC.

Ana zargin mutanen biyu da cin zarafin wani ɗan barkwanci na kafafen sada zumunta daga wani wuri da ke ɗauke da tambarin NSCDC.

Rundunar ta ce an kammala bincike kan lamarin kuma za a ɗauki matakin doka a kansu.

More from this stream

Recomended