Sanata Ali Ndume ya danganta nasarorin da yake samu a zaɓe da taimakon Allah da kuma goyon bayan al’ummar mazabarsa, yana mai cewa ba ya cikin mutanen da suke da tasiri sosai a gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.
Da yake magana a shirin Sunday Politics na gidan talabijin na Channels TV, Ndume ya ce yana shirin shiga zaɓensa na bakwai bayan ya yi wa’adi biyu a Majalisar Wakilai da kuma wa’adi huɗu a Majalisar Dattawa.
Sanatan ya bayyana cewa mutanen mazabarsa suna da wayewa da ilimi, kuma suna goyon bayansa da jam’iyyar APC ne saboda suna ganin hakan ya fi dacewa da muradunsu.
Ndume ya kuma ce duk da cewa yana daga cikin masu sukar gwamnati a wasu lokuta, yana ganin ya dace a yaba wa shugabanni idan suka aiwatar da abin da zai amfani jama’a.
Ndume: Allah Da Mutanena Ne Suka Ba Ni Tikitin APC, Ba Ni Da Farin Jini a Wajen Gwamnati

