Naftali Bennett Ya Zama Zababben Firai Ministan Isra’ila – AREWA News

VOA Hausa

Naftali Benett ya zama zababben Firai ministan Isra’ila bayan da jam’iyun adawan kasar, suka dunkule wuri guda suka kafa gwamnati.

Hakan na zuwa ne bayan da majalisar dokokin kasar ta Knesset ta kada kuri’ar amincewa da gwamnatin hadakar.

Netanyahu shi ne Firai Ministan da ya fi dadewa akan wannan mukami, inda ya kwashe shekara 12.

Jam’iyyu takwas ne suka dunkule wuri guda don kafa sabuwar gwamnati.

Wannan gwamnatin hadaka ta kawo karshen rashin tsayayyiyar gwamnati da kasar ta Isra’ila ba ta da ita, abin da ya sa aka yi zabuka har hudu cikin shekara biyu kafin a kai da kafa wannan gwamnatin hadaka.

Israeli Prime Minister Benjamin Netanyahu looks at U.S. Secretary of State Anthony Blinken (not pictured) during a joint news conference in Jerusalem, May 25, 2021.
Israeli Prime Minister Benjamin Netanyahu looks at U.S. Secretary of State Anthony Blinken (not pictured) during a joint news conference in Jerusalem, May 25, 2021.

Sabuwar gwammnatin Bennet mai ra’ayin mazan jiya, wanda dan jam’iyyar Yamina ne, za ta yi wa’adin shekara biyu.

Zai kuma mika wa Yair Lapid, shugaban masu matsakaicin ra’ayi na Yesh Atid, don ya karasa sauran shekara biyu.

Masu shari na hangen baya ga shan kaye da ya yi, Netanyahu na kuma fuskantar tuhume-tuhume kan zargin cin hanci da rashawa.

More News

Ɗalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...