‘Na sha kama mijina yana lalata da mata a kan gadona’ | BBC Hausa

Map
Image caption

Ana yawan samun rikici tsakanin ma’aurata a Najeriya

Gardamar aure kan cin amanar juna ta kai wasu ma’aurata kotu inda suka nemi a kashe aurensu.

Matar mai suna Misis Edith Obieme ta roki wata kotu a birnin Legas na Najeriya ta kashe aurenta na shekara biyu da Mista Kingsley inda ta ce ta sha kama shi yana kwanciya da mata da dama a gadonta na aure.

Tun farko mijin ne ya shigar da kara inda ya bukaci kotun ta kashe aurensu saboda acewarsa matar ta sha barazanar halaka shi, zargin da ta musanta.

Matar ta nemi kotun ta kashe auren domin yadda mijin ke kwanciya da mata a gaban idonta.

“Ya taba kwanciya da ‘yar aiki, ban taba cewa ina bukatar ‘yar aiki ba, amma a ranar da na kama shi yana kwanciya da ita, a ranar ta kwashe kayanta ta bar gidan.”

“Kingsley talaka ne, ba shi da ko kwabo, babu ribar da zan ci idan ma na kashe shi,” kamar yadda kamfanin dillancin labaran kasar NAN, ya rawaito tana fada a kotu.

“Kawai na taba barazanar zan yi wa farkarsa wanka da ruwan guba (acid) idan har na sake kama shi yana lalata da matan banza, in ji Edith wacce ‘yar kasuwa ce mai goyon yaro dan wata hudu.

Ta shaida wa kotun cewa ita ke dawainiya da hidimar gida da kula da ‘ya’yansa da matansa da ya saka suka fita suka bari.

Sai dai mijin ya shaida wa kotun cewa duk lokacin da suka samu sabani, matar kan yi barazanar cewa za ta yi ma shi wanka da ruwan guba.

“Ba na son mutuwa, kuma ina tsoron wata rana za ta aikata.”

“Na dade ba na cin abincin da ta dafa domin gudun ka da na ci guba,” in ji shi.

Dukkaninsu dai sun nemi kotu ta kashe auren, kuma bayan sauraren bahasi, kotun da ke Igando ta dage sauraren karar zuwa 18 ga Yuli.

More News

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...