Rundunar Sojin Najeriya ta ce ta ceto dalibai guda shida da masu garkuwa suka sace da safiyar Alhamis , a jihar Kaduna.
Sojojin sun ce masu garkuwar dai sun sace ‘yan matan ne a lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa makaranta.
Rundunar sojin ta ce baya ga ‘yan matan an kuma yi garkuwa da wasu ‘yan tasi guda uku, inda sojojin da ke kusa da inda abin ya faru suka bazama neman wadanda aka yi garkuwar da su bayan samun labari.
Sojojin sun ce sun samu nasarar ceto mutanen ne bayan musayar wuta da masu garkuwar inda har wani daga cikin masu satar mutanen da samu rauni, sannan kuma sauran ‘yan bindigar suka arce.
- An sace shugaban makaranta a Kaduna
- Tsoron garkuwa na sa jama’a jure wuya a tashar jirgin kasa
Wannan ne dai karo na uku da ake sace ‘yan makaranta a cikin mako guda a jihar ta Kaduna.
A ranar Alhamis ta makon da ya gabata ne dai aka sace ‘yan mata guda 6 da malamansu guda biyu daga makarantar sakandare ta kwana ta Engravers College. Kuma har yanzu ba wani labari. A ranar Alhamis din nan kuma aka sace shugaban wata makarantar fasaha a jihar ta Kaduna.