Morsi ya yi shahada – Shugaba Erdogan

Morsi

Morsi ya mutu yana da shekara 67

Kungiyar Muslim Brotherhood ta yi ikirarin cewa an hana marigayi Mohammed Morsi samun kulawar lafiya kuma an tsare shi cikin kadaici tsawon shekara shida a gidan yari.

Tsohon shugaban mai shekara 67 ya yanke jiki ya fadi lokacin sauraron bahasinsa kan zarge-zargen leken asiri a kotun birnin Alkahira.

Muslim Brotherhood ta zargi hukumomin Masar da alhaki kan mutuwarsa, yayin da Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan, ya bayyana Mursi a matsayin shahidi.

“Ganin yadda marigayin, wadda aka yi wa shari’ah a kotun juyin mulki kuma aka yanke masa hukuncin kisa, ya ja numfashinsa na karshe a kotu, hakan wata manuniya ce ta gallazawar da aka yi masa tsawon shekaru, shi da jama’arsa.


Mazauna birnin Istanbul na Turkiyya sun yi masa sallar janaza

Erdogan ya ce zai riki shugabancin kasar Masar na Abdel Fateh al-Sisi da alhaki kuma tarihi ba zai taba mantawa da ‘yan kama-karyan da suka yi sanadin mutuwar Morsi ba.

Shi ma wani dan majalisar dokokin Burtaniya na jam’iyyar Conservative, Crispin Blunt, wanda ke daya daga cikin mutanen da suka yi ta bayyana damuwa bara game da yadda ake tsare da shugaban, ya bukaci gudanar da bincike na kasashen duniya.

Ya fada wa BBC cewa halin da aka tsare Morsi ya yi muni matuka, kuma sun fada a lokacin, cewa idan ba a kula da lafiyarsa cikin gaggawa ba, hakan zai yi lahanin dindindin ga lafiyarsa, ko ma ya zama sanadin cikawarsa.

“Kuma ga shi yanzu abin da muka fada ya tabbata, don haka sai gudanar da bincike mai zaman kansa, don tantance musabbabin rasuwarsa” in ji Crispin.

Daya daga cikin masu adawa da Morsi, Khaled Dawoud na jam’iyyar National Salvation Front, ya ce ba a yi wa marigayin adalci.

A cewarsa su jam’iyya ce da ta rika kiran a mutunta doka, a mutunta hakkin dan Adam kuma ya ce ya yi imani an hanawa Morsi wasu daga cikin hakkokinsa na bil’adama ciki har da ‘yancinsa na samun kula da lafiya.

Ma’aikatar cikin gidan Masar dai ta sanya kasar cikin ta-kwana.

Rasuwar Mohammed Morsi ta zo ne ‘yan kwanaki gabanin fara gasar cin kofin Afirka da Masar ke karbar bakunci.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...