Mayaƙan ISWAP sun sace yara mata da maza 20 a Jihar Borno

Masu iĆ™irarin jihadi da ake zargin ‘yan Ć™ungiyar ISWAP ne sun kashe mutum biyu tare da sace wasu yara 20 a kusa da garin Chibok na Jihar Borno ranar Alhamis.

Wani shugaban yankin ya faÉ—a wa manema labarai cewa maharan sun afka wa garin Piyemi, inda suka yi awon gaba da mata 13 da maza bakwai.

A cewar mazauna yankin, mayaƙan na Islamic State West Africa Province (ISWAP) sun afka wa garin ne da rana cikin kakin sojoji suna harbe-harbe tare da sace kayayyakin shaguna, sannan suka dinga ƙona gidaje.

“Sun harbe mutum biyu sannan suka sace yara mata 13 da maza bakwai, shekarunsu 12 zuwa 15,” kamar yadda mazaunin yankin Samson Bulus ya faÉ—a wa AFP.

Wani mai suna Silas John ya ce “maharan sun zuba yaran 20 cikin wata motar a-kori-kura da suka Ć™wace a Ć™auyen kuma suka shiga daji da su”.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...