Matakin rufe iyakar Najeriya da kasar Benin ya dakatar da harkokin kasuwanci

Rahotannin dake fitowa daga yankin iyakar Najeriya da jamhuriyar Benin ta yankin garin Seme, na nuna cewa yanzu haka hukumomin tsaro a Najeriya sun rufe kan iyakar kasar da makwabciyarta.

Rufe kan iyakar dai ya haifar da rashin jin dadi ya kuma janyo hasarar ga ‘yan kasuwar dake kai da komo a duk rana domin saye da sayarwa.

Alhaji Faisal Ali Muhammed, shine Sarkin Hausawan garin Seme dake kan iyakar Najeriya da Benin, ya tabbatar da wannan lamari a wata hira ta wayar salula da wakilin muryar Amurka Babangida Jibrin ya yi da shi, yace bayan tarukan harkokin tsaro da suka gudanar da jami’an da aka turo daga Abuja, daga bisani an shaida masu cewar za’a rufe kan iyakar tsawon wata guda, domin tabbatar da tsaro, kuma duk da cewar lamarin ya haifar da matsaloli na kasuwanci, yana ganin da zarar an bude iyakar, komai zai daidaita.

Game da bayanin yadda matakin ka iya shafar tattalin arzikin kasashen biyu, Dr Dauda Mohammad Kontagora, ya ce akasarin kasuwancin da Najeriya ke yi da kasashe makwabtanta ana yin sa ne akan iyakar Najeriya da Jamhuriyar ta Benin, abinda kuma zai kawo cikas da koma baya.

Sai dai a cewar masanin yana ganin lamarin zai inganta kafin ma ya kai ga yin illa ga tattalin arzikin kasa.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...