Masu zanga-zanga sun lalata ofishin APC a jihar Ribas

Masu zanga-zangar matsin rayuwa  sun samu nasarar lalata ofishin jam’iyar APC a jihar Ribas.

Tun makon da ya wuce ne matasa dake faɗin ƙasarnan suka fantsama kan tituna inda suke zanga-zanga kan gwamnati ta kawo karshen matsin rayuwa da al’ummar Najeriya ke fuskanta.

Zanga-zangar ta haifar da lalata dukiyar gwamnati da ta al’umma a wurare daban-daban.

Da yakewa manema labarai jawabi a birnin Fatakwal ranar Talata shugaban riƙon jam’iyar APC a jihar ta Ribas, Tony Okocha ya ce ya yi mamakin dalilin da ya sa aka kai ofishin jam’iyar APC hari a jihar.

Okocha ya zargi gwamnatin jihar da da hannu dumu-dumu akai hari kan sakatariyar.

Ya ce suna da labari cewa ɗaukar nauyin mutanen da suka farma ofishin aka yi da kuma wanda ya ɗauki nauyinsu.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...