Malami ya ce gwamnati za ta bi umurnin kotu, amma za ta kalubalanci matakin

Gwamnatin Najeriya ta ce za ta bi umurnin da kotun kolin kasar ta bayar na dakatar da aiwatar da wa’adin daina amfani da tsofaffin kudade a kasar.

A ranar Laraba kotun kolin ta ba da umurni ga bankunan kasar da su jingine wa’adin har sai yadda karar da aka shigar ta kaya.

A farkon makon nan jihohin Kaduna, Kogi da Zamfara suka maka gwamnatin Najeriya a kotu kan shirin aiwatar da wa’adin hana amfani da tsoffin takardun kudaden 200, 500 da 1000.

Yayin wata hira da aka yi da shi a gidan talbijin na Arise TV a ranar Alhamis, Ministan Shari’a kuma babban lauyan gwamnatin tarayya, Abubakar Malami, ya ce za su bi umurnin, amma za su kalubalance shi a zama na gaba.

Da farko babban bankin Najeriya na CBN ya saka wa’adin daina amfani da tsoffin takardun kudaden akan ranar 31 ga watan Janairu.

Amma an tsawaita wa’adin zuwa 10 ga watan Fabrairu bayan korafe-korafe da jama’a ke ta yi.

Al’umar Najeriya na fuskantar karancin sabbin takardun kudaden 200, 500 da 1000 da aka sauyawa fasali, lamarin da ya haifar da dogayen layuka a bankunan kasar.

Rahotanni sun yi nuni da cewa an kai hare-hare kan wasu bankuna a wasu sassan kasar.

Bankin na CBN ya dora alhakin hakan akan masu boye kudaden don biyan bukatun kansu.

A ranar 15 ga watan Fabrairu kotun kolin za ta yi zama na gaba don ci gaba da sauraren karar.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...