A yau Laraba majalisar wakilan Nijeriya karkashin jagorancin kakakin majalisa Femi Gbajabiamila za ta gayyaci jarumin maza jan gwarzo namijin zaki DCP Abba Kyari domin a karrama shi.
Shugaban majalisar shi ya bayyana haka a zaman da suka yi, yace lokacin da ya karanta tarihin gwagwarmayar da Abba Kyari ya yi a aikin ‘dan sanda, da manyan nasarori da ya samu wajen yaki da miyagun laifuka sai ya ji ya burge shi, kuma ya cancanci majalisar kasa ta karrama shi.
Insha Allahu DCP Abba Kyari zai cigaba da samun daraja da daukaka saboda ya dogara da Allah akan gaskiya da kuma adalci ga kowa.
Yaa Allah Ka daukaka darajar DCP Abba Kyari, Ka kareshi daga dukkan sharri tare da yaransa, Ka kaishi matsayin IGP Amin.