Mai Yiwuwa A Dawo Da Tsauraran Matakai A Najeriya

VOA Hausa

Gwamnatin Najeriya ta gargadi al’ummar kasar da suyi taka tsan tsan wajen kauce wa kamuwa da cutar corona, inda take cewa rashin daukar matakai da suka dace ka iya sanya a sake killace jama’a cikin gidajensu, a kuma daidai lokacin da kungiyar hadakar ma’aikatan lafiya ta kasar ke barazanar daukar mataki idan har Gwamnatin ta kasa cika musu alkawuransu.

Sakataren gwamnatin kasar, Boss Mustapha ne ya sanar da haka, sakamakon ganin yadda cutar ke sake dawowa a kasashen da suka yi nasarar dakile ta, abinda ya sa Hukumar Lafiya ta Duniya ke dada gargadi ga jama’a akan bin matakan kariya, hakazalika hukumar takaita yaduwar cututtuka ta kasar NCDC ta ce ta na aiki tare da hadin gwiwar cibiyar nazarin lafiya ta Najeriya da takwarorinsu kan gudanar da binciken fadada sanin wadanda ke dauke da cutar a kasar.

Tsohon shugaban hukumar ta NCDC, Farfesa Abdulsalam Nasidi ya yi tsokaci kan muhimmancin wadannan matakai da kuma halin da ake ciki.

A daya bangaren kuwa bayan Kungiyar hadaka ta ma’aikatan lafiya a Najeriya, JOHESU ta dawo daga yajin aikin da ta shiga na mako guda a ranar Litinin din nan, saboda abin da ta kira rashin biyan hakkokinta da gwamnatin kasar ta yi, ya zama na baya bayan nan a matsalolin bangaren lafiyar kasar, inda a yanzu adadin wadanda suka kamu da cutar ya haura dubu 57. Kuma akwai yiwuwar kungiyar ta sake komawa yajin aikin a cewar shugaban kungiyar rashen jihar Kano Dakta Murtala Isa Umar.

Dan Majalisar Wakilan Tarayya kuma shugaban kwamitin kiwon lafiya, Dakta Yusuf Tanko Sununu, ya bayyana cewa gwamanti na iya kokarinta wajen samar da mafita.

More News

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...