Laliga: Madrid ta ci gaba da zama a mataki na uku bayan doke Villareal

Real Madrid

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Real Madrid ta yi nasarar doke Villareal 3-2 a wasan mako na 36 a gasar cin kofin La Liga da suka fafata a Santiago Bernabeu ranar Lahadi.

Real ta ci kwallayen ne ta hannun Jesus Vallejo da kuma Mariano Diaz da ya ci guda biyu, yayin da Villareal ta zare biyu ta hannun Gerard Moreno da kuma Jaume Costa.

A wasan farko da kungiyoyin biyu suka buga a gasar ta La Liga bana ranar 3 ga watan Janairu tashi suka yi 2-2.

Saura wasa biyu a kammala La Ligar shekarar nan, wadda Barcelona ta lashe kofin, kuma na 26 jumulla, inda Lionel Messi ya ci na 10 a Camp Nou.

Real tana nan a matakinta na uku da maki 68, ita kuwa Villareal ita ce ta 14 da maki 40.

Sauran wasannin da suka rage wa Madrid sun hada da zuwa gidan Sociedad ranar 12 ga watan Mayu da wasan karshe a Bernabeu da Real Betis ranar 19 ga watan nan.

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...