Kun san mazauna birnin da ke kukan wutar lantarki ta musu yawa? | BBC Hausa

Yadda taurari suke a sararin samaniya

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Taurarin subahana abin ban sha’awa

Garuruwa da birane da ke kusa da tafkin Geneva, babban birnin Switzerland sun kasance cikin duhu a wani mataki na fadakarwa da wayar da kan jama’a a kan muhimmancin sanin illar hasken fitulun lantarki.

An karkashe fitulun kan titi, sannan kuma aka shawarci mutane su ma su kashe kwayayen lantarki na gidajensu a lokacin.

Wadanda suka shirya wannan abu sun ce sakamakon ya kasance na mai ban sha’awa, yadda birnin ya kasance da duhu, a lokacin samaniya kuma ta kasance tarwal da ado na taurarin subahana, abin ba magana.

Daman tun ba yanzu ba ‘yan sama jannati a birnin na Geneva sun sha kokawa cewa ba sa iya hangen taurari a sararin samaniya saboda fitilun kan hanya da suka mamaye titunan kasar.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Tutar kasar Switzerland

Masana a bangaren muhalli sun ce illar hasken wutar lantarkin na shafar dabbobi da shuke-shuke.

An bukaci mutanen kasar miliyan guda da ke zaune kusa da tafkin na Geneva da su saki jikinsu da wannan duhun da suka kasance a cikinsa a daren domin su ganewa idanuwansu yadda yanayin taurari ya ke da daddare a sararin samaniya.

Sai dai saboda dalilai na tsaro, ba a jefa birnin na Geneva gaba daya cikin duhun ba, sannan an bukaci masu tafiya a kafa da masu tafiya a kekuna da su sanya kayan da za a iya ganinsu a hanya don gudun kada a kade su da abin hawa ko su yi karo da juna.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...