Wata kotu da ke Abuja, babban birnin Najeriya, ta yankewa Hon. Farouk Lawal hukuncin zaman gidan yari har na tsawon shekara bakwai.
Lawal shi ne tsohon shugaban kwamiti a Majalisar wakilai da ke sa ido kan harkar kudaden tallafin mai a Najeriya.
Wannan hukunci na zuwa ne, bayan da kotun ta same shi da laifin neman cin hancin dala miliyan uku daga wajen hamshakin mai kudin nan Femi Otedola, a lokacin ana bincike kan kudaden tallafin mai a shekarar 2012.
Lawal shi ne tsohon shugaban kwamiti a Majalisar wakilai da ke sa ido kan harkar kudaden tallafin mai a Najeriya.
Wannan hukunci na zuwa ne, bayan da kotun ta same shi da laifin neman cin hancin dala miliyan uku daga wajen hamshakin mai kudin nan Femi Otedola, a lokacin ana bincike kan kudaden tallafin mai a shekarar 2012.