Kotun sauraron kararrakin zabe a garin Lokaja na jihar Kogi ta soke zaben Sanata Dino Melaye, wanda yake wakiltar shiyyar Kogi ta Kudu a Majalisar Dattawan Najeriya.
Yayin zaman kotun na ranar Juma’a ne aka soke zaben kuma aka umarci sake sabon zabe a shiyyar.
Daya daga cikin mutanen da suka kalubalanci Mista Melaye ne wato Sanata Smart Adeyemi na jam’iyyar APC ya shigar da kara a gaban kotun.
Bayan yanke wannan hukuncin Sanata Melaye ya bukaci magoya bayansa da su kwantar da hankalinsu, inda ya ce zai daukaka kara zuwa gaba.
Sanata Melaye ya fara zama dan majalisar wakilan kasar ne a shekarar 2007, inda yake wakiltar mazabar Kabba da Ijumu da ke jihar Kogi.
Sai da ya yi wa’adi biyu a majalisar wakilai kafin ya lashe zaben dan majalisar dattawa a shekarar 2015.
Kazalika a watan Yuni ne ya bayyana muradinsa na shiga takarar neman gwamnan jihar Kogi, wanda za a yi a watan Nuwamba mai zuwa.