Katsina: ‘Yan bindiga sun harbi mai garin ‘Yandaka, sun yi awon gaba da iyalansa

A daren Asabar din ta gabata ne, ‘yan bindiga dauke da manyan bindigogi suka harbi Maigarin Yandaka, da ke cikin Karamar Hukumar Batsari, Alhaji Shehu Iliyasu. Inda suka harbe shi a tsakiyar kansa da kuma hannunsa. Kuma suka sace matarsa da ‘ya’yansa guda uku suka tafi da su.

An yi gaggawar kai shi asibitin Katsina, domin cire masa harsashen dake cikin kansa da hannu, inda aka wuce da shi asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano, yanzu haka yana can kwance.

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Katsina, ta tabbatar da afkuwar wannan hari da aka kai garin Yandaka, dake cikin karamar hukumar Batsari ta bakin mai magana da yawun rundunar SP Gambo Isa.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...