Karin Mutum 187 Sun Kamu Da COVID-19 a Najeriya

VOA Hausa

Gaba dayan adadin wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar COVID-19 a Najeriya ya kai 58,647 zuwa daren Talata, 29 ga watan Satumba, a cewar hukumar NCDC da ke sa ido kan cututtuka masu yaduwa.

A bayanan da ta ke fiddawa a kowace rana a shafinta na Twitter, hukumar ta NCDC ta ce an samu karin mutum 187 da suka kamu da cutar a ranar.

A cewar hukumar, cikin mutum 58,647 da suka kamu da cutar, mutum 49,937 sun warke kuma an sallame su daga asibiti yayin da mutum 1,111 ne suka mutu.

Hukumar ta kuma ce an samu karin adadin ne daga jihohi 13, ciki har da Jihar Legas da mutum 74. Sai kuma jihar Filato da ke biye da mutum 25.

Sauran jihohin sun hada da Rivers (25), Gombe (19), FCT (19), Osun (10), Kaduna (5), Borno (3), Ogun (2), Katsina (2), Nasarawa (1), Bayelsa (1), Edo (1)

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...