Kanar Goita zai jagoranci gwamnatin Mali | Labarai

Hakan na nufin cewar, Kanar Goita zai jagoranci Malin, a yayin da ake shirin sake mayar da ita turbar demokradiyya, bayan kwace mulkin kasar da yayi a wannan mako mai karewa.
Kotun tsarin mulki ta bayyana cewar, ta zartar da hakan ne domin rufe gibin rashin shugaban kasa, bayan murabus na shugaban rikon kwarya Bah Ndaw.
A ranar Litinin ne dai, dakarun kasar suka capke tare da tsare Ndaw da framinista Moctar Ouane, kafin sakinsu ranar Alhamis bayan sun sanar da yin murabus daga mukamansu.
Kafin hambarar da gwamnatin nasu dai, Ndaw da Ouane na jagorantar gwamnatin riko, bayan kifar da mulkin zababben shugaba Boubacar Keita a watan Augustan bara.

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...