Kalli hotunan barnar da rikicin ‘yan Shi’a da ‘yan sanda ya haifar | BBC Hausa

Hakkin mallakar hoto
KOLA SULAIMON

Wani dan sanda na tafiya a gefen wata mota da masu goyon bayan shugaban Kungiyar ‘Yan Uwa Musulmi, Sheikh Ibrahim Zakzaky suka kona a kusa da harabar majalisar dokokin Najeriya a Abuja, babban birnin kasar ranar 9 ga watan Yulin 2019.

Hakkin mallakar hoto
KOLA SULAIMON

Masu goyon bayan shugaban ‘yan Shi’an da ke tsare sun yi arangama da jami’an tsaro kuma mutane da yawa sun samu raunuka ciki har da ‘yan sanda biyu kamar yadda hukumomi da shaidu suka bayyana.

Hakkin mallakar hoto
KOLA SULAIMON

‘Yan kwana-kwana na kokarin kashe wutar da ke fitowa daga wata mota bayan arangamar tsakanin jami’an tsaro da magoya bayan Sheikh Ibrahim Zakzaky.

Hakkin mallakar hoto
KOLA SULAIMON

Mummunar arangamar ta jikkata mutane. Wani takalmi a wurin da jini ya zuba yayin rikicin tsakanin jami’an tsaro da mabiya Ibrahim Zakzaky.

Hakkin mallakar hoto
KOLA SULAIMON

An lalata motoci da gine-gine a lokacin taho-mu-gaman. Nan wani wurin tsayuwar ‘yan sanda ne da masu zanga-zangar suka lalata ranar 9 ga watan Yulin 2019.

Hakkin mallakar hoto
KOLA SULAIMON

Kungiyar ‘Yan Uwa Musulmin dai sun musanta zarge-zargen rundunar ‘yan sanda na cewa magoya bayan Ibrahim Zakzaky sun harbi ‘yan sandan uku. Wannan wata motar ‘yan sanda ce da masu zanga-zangar suka lalata.

Hakkin mallakar hoto
KOLA SULAIMON

Wani wurin duba motoci da masu zanga-zangar suka lalata sannan suka yi rubutun nuna kin jinin tsare shugaban kungiyarsu Ibrahim Zakzaky.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...