Iran Ta Yi Barazanar Mayar Da Martani Kan Matakan Amurka A Mashigar Hormuz



Dakarun tsaron Iran sun yi barazanar ɗaukar matakin ramuwar gayya idan Amurka ta ci gaba da datse tasoshin ruwanta a mashigar Hormuz.

Rahotanni daga kafofin yaɗa labarai na Iran sun ambato wata sanarwa daga rundunar sojin ƙasar, wadda ta ce za su mayar da martani idan aka ci gaba da hana zirga-zirgar jiragen ruwansu.

Wannan na zuwa ne bayan da Amurka ta kama wasu jiragen ruwan Iran, biyo bayan matakin da ta fara ɗauka na rufe tasoshin ruwan ƙasar tun daga ranar 13 ga watan Afrilu.

Lamarin na ƙara tayar da hankula a yankin, yayin da ake fargabar ƙara tsananta rikici tsakanin ƙasashen biyu.

More from this stream

Recomended