Ina Neymar, Eriksen, Varane, Vorm, Mustafi, Ibe, Bravo za su tafi? | BBC Sport

Neymar

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Juventus ta fara farautar Neymar

Barcelona na shirin karbar aron Neymar mai shekara 27 daga Paris St-Germain a wannan makon da nufin sayen dan wasan idan an sake bude kasuwar musayar ‘yan wasa. (ESPN)

Juventus ta shiga sahun manyan kungiyoyin da ke bukatar Neymar, inda ta fara tattaunawa da PSG domin karbar dan wasan na Brazil. (AS)

Barcelona ba ta shirya yin watsi da burin dawo da Neymar ba a Camp Nou. (Marca).

PSG ta fi son ta ba Real Madrid Neymar don ta karbi dan wasan baya na Faransa Raphael Varane, mai shekara 26, da kuma matashin dan wasa Vinicius Jr. (Telefoot, via Sun)

Dan wasan Tottenham na Denmark Christian Eriksen, mai shekara 27, ya ce yana sha’awar komawa Barcelona ko Real Madrid ko Juventus. (ESPN)

Arsenal za ta bar dan wasan Jamus Shkodran Mustafi, mai shekara 27 ya koma Roma a matsayin dan wasan aro amma da nufin sayar da shi kan fam miliyan £23m. (Forza Roma, via Sun)

Golan Chile Claudio Bravo, mai shekara 36 zai bar Manchester City a karshen kaka. (Sun)

Ole Gunnar Solskjaer ya nanata cewa Paul Pogba, mai shekara 26, ba zai bar Manchester United ba. (Sky Sports)

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...