Gwamnatin jihar Zamfara ta sanar da fara biyan kuɗaɗen garatuti ga masu ritaya na rukuni na huɗu ƙarƙashin tsarin shekarar 2024 zuwa 2025.
A wata sanarwa da Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Al’adu ta jihar ta fitar, ta ce gwamna Dauda Lawal ne ya umarci ofishin Akanta Janar da ya fara biyan kuɗaɗen nan take.
Sanarwar ta bayyana cewa matakin na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na inganta walwalar tsofaffin ma’aikatan gwamnati tare da tabbatar da sun samu haƙƙoƙinsu ba tare da jinkiri ba.
Gwamnatin ta ce tana daraja gudunmawar da masu ritaya suka bayar wajen ci gaban jihar, kuma za ta ci gaba da ba da fifiko ga jin daɗinsu.
Haka kuma ta buƙaci waɗanda sunayensu ke cikin rukuni na huɗu da su haɗa kai da hukumomin da abin ya shafa domin sauƙaƙa karɓar kuɗaɗensu.
Gwamnatin ta kuma gode wa masu ritaya bisa haƙuri da goyon bayan da suke bayarwa yayin da ake ci gaba da warware sauran basussukan fansho da garatuti.
Gwamnatin Zamfara Ta Fara Biyan Garatutin Masu Ritaya

