Gwamnatin Oyo ta rushe gidan da aka ɓoye waɗanda aka yi garkuwa da su

Gwamnatin jihar Oyo a ranar Litinin ta rushe wani gida da masu garkuwa da mutane su ka ta yi amfani da shi wajen ɓoye yar uwar tsohon ministan wutar lantarki Bayo Adelabu da aka yi garkuwa da ita tare da ƴaƴanta biyu.

Jami’an yan sanda ne suka samu nasarar kuɓutar da matar da ƴanyanta biyu tagwaye dake da shekaru 12 daga gidan da ake tsare da su.

Binciken da gwamnati ta gudanar ya nuna cewa anyi amfani da gidan a matsayin wata maɓoya da masu garkuwar ke amfani da ita.

Ma’aikatar ƙasa da gidaje ce jihar tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro ne suka gudanar da aikin rushe gidan.

More from this stream

Recomended