Gwamnatin Najeriya ta fara biyan malaman jami’o’i bashin da suke bi

Gwamnatin tarayya ta fara biyan albashin malaman jami’o’in da aka riƙe a karkashin kungiyar malaman jami’o’i.

Majiyoyi da dama a bangaren ilimi sun tabbatar wa manema labarai a Abuja sabon lamarin a ranar Litinin.

Shugaban ASUU na Jami’ar Fasaha ta Tarayya da ke Minna, Farfesa Gbolahan Bolarin, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce, “Eh gaskiya ne.  An fara biyan kuɗi.”

A watan Oktoban 2023 ne dai shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da sakin albashin hudu daga cikin watanni takwas na ASUU da gwamnati ta hana a baya.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]