Gwamnatin Najeriya Ta Cire Harajin VAT, Inda Abinci, Kaya, Motoci Za Su Yi Araha A Wannan Shekarar – AREWA News

Kudirin tattalin arziki na shekarar 2020, ya zo da sababbin manufofi da ake sa ran za su jawowa Najeriya kudin shiga tare da zabubar da tattalin kasar, kamar yadda Jaridar The Cable ta ruwaito.

Jadawalin Wasu daga cikin amfanun wannan sabuwar dokar da ake kyautata zaton talakawan kasar Nijeriya zasu sha jarmiya.
👇👇👇

1. Motoci za su rage tsada, an dawo da harajin shigo da motoci 5% daga 35%.

2. Babu haraji a kan duk ma’aikatan da albashinsu bai wuce N30, 000 ba.

3. An daina cire wani kaso da sunan kudin hatimi idan aka aika kudi a banki. Wanda aka aikawa kudin da suka kai akalla N10, 000 ne zai biya N50.

4. An rage kudin harajin da ake karba a kan kananan kamfanonin da jarinsu bai kai Naira miliyan 25 ba.

5. Gwamnati za ta karbi aron kudin da aka manta da su a cikin banki kafin wanda ya mallake su ya dawo kansu.

6. Babu VAT a kan abincin dabbobi, kayan aikin gona jiragen sama na kasuwanci da sauran kayan jirgi.

Haka zalika babu VAT a kan kudin tafiya a jirgi. Gwamnati ta cire VAT a kan filaye da gidajen da aka saida.

7. Za a rika karbar haraji a ribar da aka samu daga gudumuwa ko kyauta da gwamnati ta bada.

8. An rage mafi karancin harajin da ake karba a hannun kamfanoni daga 0.5% zuwa 0.25%.

9. Kamfanonin ketare za su bukaci lambar TIN, kuma za su rika biyan haraji.

10. Za a dauke biyan haraji daga kamfanonin da ke aikin gona da noman dabbobi da kifi.

More News

Sojan Jamhuriyar Nijar sun kama Gawurtaccen Ɗan Fashin dajin Najeriya Kachalla Mai Daji

Dakarun sojan Jamhuriyar Nijar sun samu nasara kama gawurtaccen ɗan fashin dajin nan mai suna Kachalla Mai Daji a garin Illela dake kan iyakar...

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraɗiyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...