Gwamnatin Kano ta yi wa ma’aikata ƙarin girma

Hukumar da’ar ma’aikata ta jihar Kano ta amince da karin girma ga manya da kananan ma’aikata 118 a ma’aikatu da sassa da hukumomi 13.

Shugaban hukumar Dr Umar Shehu Minjibir ne ya bayyana hakan bayan zaman hukumar a Kano.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan wayar da kan jama’a na hukumar Musa Garba ya fitar jiya.

Dokta Minjibir ya ci gaba da cewa adadin wadanda aka yi wa karin girma tun bayan kaddamar da hukumar da ya jagoranta a watan Agustan wannan shekara sun kai 379.

A yayin da yake yabawa da jajircewar ma’aikatan a fadin hukumar, shugaban ya yi kira ga ma’aikatan da aka kara musu girma da su maida hankali wajen yin aiki tukuru domin samun sakamako mai kyau.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]