Gwamnati Ta Ba Da Shawara A Jingine Hawan Sallah

Kwamitin da shugaban kasa ya kafa don yaki da cutar coronavirus, ya nemi jihohi shida hade da babban birnin tarayya na Abuja, da su zauna cikin shirin kar-ta-kwana saboda yaduwar cutar coronavirus.
Kazalila kwamitin ya ba da shawarar a jingine bukukuwan hawan sallah da aka saba yi.
Cikin wata sanarwa da shugaban kwamitin, Boss Mustapha ya fitar kamar yadda kafafen yada labaran Najeriya suka ruwaito, Sakataren gwamnatin tarayyan ya zayyana jihohin Legas, Oyo, Rivers, Kaduna, Kano da Filato a matsayin wadanda aka yi masu garagdin su zauna cikin shiri.
Kwamitin har ila yau cikin sanarwar wacce aka fitar a ranar Lahadi, ya nemi sauran jihohin kasar da su kara tsaurara matakai yayin da Najeriyar ke shirin fuskantar barazanar tashin cutar a karo na uku.
Gwamnati har ila yau ta yi kira ga Musulmi da ke shirye-shiryen bukukuwan sallah, da su yi takatsatsan wajen yin shagulgulan sallar, inda ta nemi da a rarraba gudanar da sallar Idi zuwa wasu masallatan Juma’a.
A ranar 8 ga watan Yuli cibiyar da ke yaki da yaduwar cututtuka ta NCDC a Najeriya, ta sanar da bullar sabuwar cutar ta COVID-19 nau’in Delta, wacce masana suka ce ta na da saurin yaduwa.
Izuwa ranar 18 ga watan Yuli, mutum 169, 329 aka tabbatar sun kamu da cutar a Najeriya yayin da 2,126 suka mutu.

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...