Gareth Bale zai buga fafatawar Real Madrid da Eibar

Gareth Bale

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Gareth Bale

Gareth Bale zai iya buga wasan da Real Madrid za ta yi a Gasar La Liga inda za ta fafata da Eibar ranar Lahadi.

Fitaccen dan wasan na Wales yana cikin ‘yan wasa 23 da Zinedine Zidane jera domin sanya su a wasa a yayin da Real, wacce ke matsayi na biyu a saman tebur za ta karbi bakuncin Eibar wacce ke cikin kungiyoyin da ke kasan teburin.

An ajiye Bale a benchi a wasan da Real ta doke Real Betis da 2-1 ranar 8 ga watan Maris kafin a dakatar da Gasar La Liga.

Tsohon dan wasan Chelsea Eden Hazard ya dawo kan ganiyarsa bayan raunin da ya yi a gwiwarsa a watan Fabrairu.

An koma buga Gasar La Liga ba tare da ‘yan kallo ba ranar Alhamis bayan an dakatar da ita tsawon wata ukusakamakon annobar korona.

Real Madrid tana da sauran wasa 11 kuma tana bayan Barcelona da maki biyar, wacce ta yi nasara a kan Saturday’s win over Mallorca. ranar Asabar.

“Muna da sauran wasanni 11 a gabanmu kuma za mu yi bakin kokarinmu domin lashe gasar La Liga,” in ji Zidane.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...