An samu gagarumin gangami na jama’a da suka halarci taron kaddamar da wata sabuwar jam’iyyar siyasa da wani fitaccen malamin addinin Musulunci, Mahamoud Dicko, ya kafa a Bamako, babban birnin kasar Mali.
Sheik Mahamoud ya dauki wannan mataki ne na shiga fagen siyasar kasar a yayin da jama’a ke komowa daga rakiyar gwamnati a sakamakon tabarbarewar tsaro a kasar ta Mali.
Malamin wanda sananne ne a Mali, shekara goma yana jagorancin majalisar harkokin addinin Musulunci ta kasar.
A yayin kaddamar da sabuwar jam’iyyar, Mahamoud Dicko , ya yi Allah-wadai da abin da ya kira mummuna mulki na inna-naha,, sannan kuma ya lashi takobin yakar wadanda ya ce sun ci amanar al’ummar Mali.
Duk da ya ce ba zai tsaya takarar neman wani mukami ba, amma ana ganin zai iya ci gaba da zama barazana ko kuma mai tasirin sauya al’amura a siyasar kasar ta Mali.
Da farko dai malamin addinin Musuluncin mai goyon bayan shugaban kasar na yanzu ne, Ibrahim Boubacar Keïta, to amma sannu a hankali ya zamo mai sukar shugaban, yana kuma kira da a koma ga abin da ya kira akida ko tsarin dabi’u na Musulunci na ainahi da aka sani.
Ibrahim Boubacar Keita ya kama mulki a watan Satumba na 2013, tare da alkawarin hada kan kasar bayan rikice-rikice daban-daban da suka hada da na ‘yan tawaye da juyin mulki da kuma masu tayar da kayar baya na Musulunci, wadanda ke ikirarin Jihadi.
Haka kuma Sheik Mahamoud Dicko a baya ya rika suka ga ‘yancin ‘yan luwadi da madigo da dangoginsu.
A wata alama da ke nuna cewa an dauke shi ko abin da yake fada da muhimmanci, a ranar Juma’a kotun tsarin mulki ta kasar ta Mali, ta fitar da wata sanarwa, wadda a cikinta take gargadin kafa wata jam’iyyar siyasa bisa akidar kabilanci ko addini.