FIFA: Da yiyuwar a mayar da gasar cin kofin duniya duk bayan shekara biyu

Akwai masu ra'ayin cewa FIFA na son yin garambawul din ne da nufin samun ƙarin kudin shiga
Akwai masu ra’ayin cewa FIFA na son yin garambawul din ne da nufin samun Æ™arin kudin shiga

Hukumar ƙwallon ƙafa ta duniya FIFA na shirin gudanar da wani zama ta intanet, don yin garambawul a gasussukan ƙwallon ƙafa na maza da na mata.

Daga cikin muhimman abubuwan da za a tattauna akwai batun mayar da buga gasar cin kofin duniya duk bayan shekara biyu a maimakon shekara huÉ—u.

A cewar sanarwar da FIFA ta fitar ”mafi rinjayen mambobi sun aminta da yin garambawul ga jadawalin wasannin maza da na mata.”

Tuni FIFA ta kafa kwamitin da zai tattauna garambawul ɗin, a ƙarƙashin daraktan kula da ci gaban ƙwallo a duniya wato Arsene Wenger, da kuma takwararsa a bangaren mata Jill Ellis.

Sai dai kuma hukumomin da ke wakilitar nahiyoyi kamar hukumar shirya ƙwallon ƙafa ta Turai wato UEFA da kuma CAF ta Afrika da kuma Conmebol ta kudancin Amurka, sun nuna adawa da buga wasan cin kofin duniya duk bayan shekara biyu.

A cewar mai horar da tawagar Æ™wallon Æ™afa ta matan Ingila Sarina Weigman ” idan a ka yi haka ba a tausaya wa yan Æ™wallo ba.”

Ta Æ™ara da cewa ”akwai gasussuka masu Æ™ayatarwa a Turai, ga gasar Olympics sannan kuma uwa uba gasar cin kofin duniya.”

”Idan a ka ce za a riÆ™a buga waÉ—annan gasussuka masu muhimmanci kusa da kusa yaushe a ke so Æ´an Æ™wallo su huta?” Inji Weigman.

A nata ɓangaren ƙungiyar masu horar da ƴan wasa ta Turai AEFCA ta rubuta wa UEFA takardar nuna goyon bayanta kan hawa kujerar naƙi.

Akwai masu ra’ayin cewa FIFA na son yin garambawul É—in ne da nufin samun Æ™arin kudin shiga.

To amma wani bincike da a ka gudanar ya nuna cewa mafi yawan masoya Æ™wallon Æ™afa a faÉ—in duniya na sha’awar a riÆ™a buga gasar cin kofin duniya É“angaren maza duk bayan shekara biyu.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...