Akalla mutum biyu sun rasa rayukansa wasu 31 suka jikkata yayin da wasu ma’aikata biyar kuma suka bata, sakamakon wata fashewar da ta auku a wani kamfanin harhada sinadarai a birnin Leverkusen da ke yammacin Jamus.
Sinadarai masu hadari ga lafiya sama da dubu biyar ne ake hadawa a cibiyar da gobarar ta tashi a cikinta da safiyar Talata. Gobarar ta kuma kama wani defon mai da ke kusa da wajen.
Hukumar da ke kare jama’a daga bala’o’i a Jamus, ta bayyana hadarin a matsayin wata babbar barazana tare da bukatar mazauna kewayen yankin na Leverkusen da su kasance cikin dakuna, sannan a rurrufe kofofi gami da tagogi.
Akwai ma wata cibiyar makamanciyar wannan da ta kusa yin bindiga, sai dai jami’an kwana-kwana sun ce sun shawo kanta.