El-Rufai ya tunɓuke sarakuna biyu da kuma dagatai huɗu

Gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasiru El-Rufai ya amince da tsige sarakuna biyu a jihar.

Sarakunan da aka tsige sun haɗa da Mai Martaba Jonathan Paragua Zamuna na masarautar,Piriga da Mai Martaba Genaral Aliyu Ilyah Yamma na masarautar Arak.

Kwamishiniyar ƙananan hukumomi ta jihar, Hajiya Umma Ahmad ita ta bayyana haka cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin.

A cewar sanarwar daga ranar Litinin sarakunan sun tashi daga matsayinsu.

Ana zargin Gen.Iliyah Yamma da laifin naɗa dagatai huɗu waɗanda ba sunansu gwamnatin jihar ta amince da su ba da kuma rashin zama a masarautar sa.

Shi kuwa Jonathan Damuna an cire shi ne daga mulki biyo bayan rikici da aka samu a masarautar sa tsakanin al’ummomin Gure da Kitimi dake masarautar ta Piriga dake karamar hukumar Lere.

Har ila sanarwa ta ce an cire dagatan ƙauyukan Aban, Abujan Mada da kuma Anji dake masarautar Arak.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...