EFCC Ta Kama Yan China 13 Da Laifin Haƙar Ma’adanai Babu Bisa Ka’ida Ba

Hukumar EFCC dake yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati ta ce jami’anta sun kama wasu yan kasar China 13 kan zargin hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a jihar Kwara.

A wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafin ta na Twitter a ranar Alhamis ta ce mutanen da aka kama a unguwar GRA dake Ilorin sun hada da maza 12 da kuma mace daya.

Kamen da ofishin shiyar hukumar na Ilorin ya yi an yi shi ne biyo bayan gamsassun bayanai sirri akan ayyukansu da suka haɗa da hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba da kuma kin biyan kudin haraji ga gwamnatin tarayya kamar yadda doka ta tanada.

Mutanen da aka kama sun haɗa da Guo Ya Wang ( shekaru 36), Lizli Hui (shekaru 42), Guo Jian Rong (shekaru 36), Lizh Shen Xianian (shekaru 37), Lishow Wu (shekaru 26), Guo Pan (shekaru 38), Lia Meiyu (shekaru 53), Guo Kai Quan (shekaru 36) Lin Pan (shekaru 50).

Sauran su ne Ma Jan (shekaru 38), Wendy Wei Suqin (shekaru 31), Li Zhinguo Wei (shekaru 29), and Xie Zhinguo (shekaru 53).

“Bayan da aka yi musu tambayo yi sun amsa cewa su ma’aikatan kamfanin China ne da aka fi sani da W. Mining Global Service Limited dake Olayinka a karamar hukumar Ifelodun ta jihar.” a cewar sanarwar.

Har ila yau binciken ya bayyana cewa wasu daga cikin su basu da shedar yin aiki a Najeriya sun shigo kasar ne da biza ta ziyara.

More News

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraɗiyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...