EFCC Ta Kama Mutane 20 Kan Zargin Laifukan Zabe A  Abuja

Hukumar Economic and Financial Crimes Commission (EFCC) ta kama mutane 20 bisa zargin aikata laifukan zabe a yayin zaben kananan hukumomi da aka gudanar a Federal Capital Territory.

Mai magana da yawun hukumar, Dele Oyewale, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da aka fitar a Abuja ranar Lahadi.

Ya ce an kama wadanda ake zargin ne a sassa daban-daban na birnin bisa laifuka da suka hada da sayen kuri’u, sayar da kuri’u da kuma hana jami’an zabe gudanar da aikinsu. Ya kara da cewa an kama kudade har naira miliyan 17.2 a hannunsu.

A cewarsa, an kama daya daga cikin wadanda ake zargin da kudi naira miliyan 13.5 a cikin mota da aka ajiye kusa da rumfar zabe a karamar hukumar Kwali.

Ya kara da cewa za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu bayan an kammala bincike.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]