Hukumar EFCC dake yaĆ™i da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati ta titsiye tsohuwar ministar harkokin mata Pauline Tallen kan zargin azurta kai ta hanyar al-mundahana.
Jaridar The Cable ta gano cewa, Tallen ta isa ofishin EFCC dake Abuja a ranar Juma’a domin amsa tambayoyi kan al-mundahanar kuÉ—in da ya kai naira biliyan biyu.
Duk da cewa kawo yanzu babu cikakkun bayanai kan zarge-zargen da ake mata wata majiya dake hukumar ta EFCC ta ce ana zargin tsohuwar ministar da karkatar da kudaden da suka shafi taron kungiyar matan shugabannin kasashen Afirka kan zaman lafiya da ake kira African First Lady Peace Mission Project (AFLPM) a turance.