DSS: Zamu bi umarnin kotu wajen sakin El-zakzaky

Hukumar tsaro ta farin kaya wato DSS ta ce zata bi umarnin kotu da ya bawa shugaban kungiyar shi’a a Najeriya, Sheikh Ibrahim Elzakzaky damar zuwa kasar Indiya domin a duba lafiyarsa.

Wata babbar kotu dake Kaduna ita ce ta bayar da umarnin ranar Litinin biyo bayan bukatar da babban lauya, Femi Falana( SAN) ya shigar gabanta.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin mai magana da yawun hukumar, Peter Afunaya ya tabbatar da cewa hukumar ta karbi sakon umarnin kotun.

Ya kara da cewa hukumar na hada kai da hukumomin da suka da ce wajen ganin an tabbatar da bin umarnin bisa sharudan da kotun ta gindaya

Kotun ta bawa Elzakzaky izinin tafiya kasar Indiya a duba lafiyar sa bisa wasu sharuda da suka hada da rakiya daga jami’an hukumar ta DSS da kuma na gwamnatin jihar Kaduna.

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...