DSS ta saki Omoyele Sowore

A

Hakkin mallakar hoto

Hukumar tsaro ta farin kaya a Najeriya DSS ta saki Omoyele Sowore bayan ya yi fiye da wata uku a hannunta, kamar yadda lauyansa Femi Falana ya tabbatar wa da BBC.

Tun da farko dai babbar kotun tarayya da ke Abuja ce ta bai wa hukumar tsaro ta DSS umarnin yin hakan a ranar Alhamis, inda ta ce a sake shi cikin sa’a 24 tare da biyansa diyyar naira ₦100,000.

Mai shari’a Ijeoma Ojukwu ta ce umarnin ya biyo bayan kin bin umarnin kotu ne da DSS din ta yi na sakin Omoyele Sowore, wanda aka bayar tun 6 ga watan Satumba.

Har ila yau ta ce ba zai yiwu hukumar DSS ta mayar da kanta kamar kotu ba, sannan kuma ta bayar da umarnin sakin abokin shari’ar Sowore mai suna Olawale Bakare.

Hukumar DSS ta ce ta tsare Sowore ne saboda zarginsa da yunkurin kifar da gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari sakamakon kiran juyin juya hali da ya yi – ya yi masa lakabi da #RevolutionNow.

Omoyele Sowore shi ne mawallafin jaridar Sahara Reporters da ake wallafawa a intanet.

Daga cikin laifukan da ake zarginsa da su har da tsokanar Shugaba Buhari a shafukan sada zumunta.

More News

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

Sojoji sun gano masana’antar Æ™era bom a jihar Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun gano wata masana'anta da mayaƙan kungiyar ISWAP suke ƙera bama-bamai. Masana'antar ƙera bama-bamai an gano ta ne a Abulam-BUK dake...

Atiku ya ziyarci Abdul Ningi

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya ziyarci dakataccen ɗan majalisar dattawa sanata, Abdul Ningi dake wakiltar mazaɓar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa. Atiku...