Dan majalisar wakilai na jam’iyyar PDP daga Gombe ya koma APC

Inuwa Garba mamba dake wakiltar mazabar Yamaltu Deba a majalisar wakilai ta tarayya ya sauya sheka daga jam’iyyar PDP ya zuwa APC abun da ake ganin zai karawa APC ƙarfi a jihar Gombe.

Gwamnan jihar Gombe, Muhammad Inuwa Yahaya shi ne ya karbi Garba a gidan gwamnatin jihar dan majalisar ya nunawa gwamnan katinsa na jam’iyar APC da ya karɓa a mazaɓarsa ta Lubo dake ƙaramar hukumar Yamaltu/Deba abun da ke nuna cewa ya zama cikkaken dan jam’iyyar APC.

Da yake bayyana dalilinsa na sauya shekar dan majalisar ya alakanta haka da shugabanci nagari da kuma mulkin ciyar da al’umma gaba na gwamnatin gwamna Inuwa Yahaya tare da kuma tsare-tsaren cigaba da gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu take yi.

A cewar sa salon mulkin jam’iyar APC a matakin jiha da kuma tarayya  ya yi dai da irin  fatan da yake da shi na samar da cigaba cikin sauri ga al’ummar mazaɓarsa.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]