Dan majalisar tarayya ya yi hatsari akan hanyarsa ta zuwa Abuja

Mamba a majalisar wakilai ta tarayya kuma tsohon kakakin majalisar dokokin jihar Edo da ya sauka, Marcus Onobun yayi hatsarin mota a ranar Laraba.

Hatsarin ya faru a wajejen Ekpoma-Auchi a babbar hanyar Benin zuwa Abuja a lokacin da dan majalisar ke hanyarsa ta komawa Abuja.

Tun da farko Onobun ya yin shirin hawa jirgi ne zuwa Abuja amma sai ya makara bai samu ba hakan yasa ya yanke shawarar tafiya a mota.

Dan majalisar dake wakiltar kananan hukumomin Esan West, Esan Central da kuma Igueben ya samu rauni a hatsarin.

Shugaban jam’iyar PDP na jihar Edo, Tony Aziegbemi ya tabbatar da faruwar hatsarin.

Ya ce Onubun na cigaba da samun kulawar likitoci a asibitin koyara na Jami’ar Benin.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]