Dalilin Da Ya Sa Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Gidan Yarin Kuje – AREWA News

VoA Hausa

Shugaban kungiyar IPOB da ke fafutukar ballewa daga Najeriya Nnamdi Kanu, ya nemi kotu ta mayar da shi gidan yarin Kuje da ke Abuja, babban birnin kasar.
A karshen watan Yuni hukumomin tsaron Najeriya suka kamo Kanu daga kasar waje aka sake gurfanar da shi a gaban kuliya.
Lauyansa Ifeanyi Ejiofor ya shigar da wata bukata a ranar Laraba a gaban kotu inda ya nemi a mayar da shi gidan yari da ke Kuje daga ofishin hukumar DSS, saboda a cewarsa, ana gana masa azaba a kaikaice, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
Lauyan ya kara da cewa likitocin da ke kula da lafiyarsa a ofishin na DSS ba su wadatar ba.
A shekarar 2015 aka fara tuhumar Kanu da laifin cin amanar kasa da wasu laifuka masu yawa, amma an ba da belinsa a shekarar 2017.
Kanu dai ya yi ikirarin cewa ana yi wa rayuwarsa barazana ne a lokacin da sojoji suka kai wani samame gidansa, lamarin da ya sa ya tsere daga kasar.
Sai dai lauyansa Ejiofor ya kara da cewa, tun da aka shigo da Kanu cikin Najeriya “ta barauniyar hanya” aka ajiye shi a wani kebabban wuri na kadaici.
Ejiofor ya kuma ce, idan ba a yi hattara an kai masa dauki ba, ran Kanun zai iya salwanta kafin a je yi masa shari’a.
Jaridar Vanguard ta ambato lauyan yana neman kotun har ila yau ta ba likitocin Kanun dama domin su gudanar da cikakken bincike kan lafiyarsa.
Bayan da aka dawo da shi Najeriya, Mai Shari’a Binta Nyako ta ba da umarnin a tsare Kanu a ofishin hukumar tsaro ta DSS har sai zuwa ranar 26 ga watan Yuli da za a ci gaba da shari’ar.
(DailyPost)

More News

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraɗiyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...