Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce ya yi mamakin rashin biyan ‘yan wasan Super Eagles kudadensu na alawus a gasar cin kofin Afirka ta Masar 2019.
Tun kafin wasan Najeriya da Guinea takaddama ta kaure tsakanin ‘yan wasan da Hukumar Kwallon Kafar kasar kan rashin biyansu kudaden ladan wasa kimanin dala 10,000 (Naira miliyan 3,600,000) kowanne.
Gwamnan Filato Simon Lalong ne ya gabatar da korafin ‘yan wasan ga Buhari a ganawar da suka yi a fadar shugaban kasa a Abuja bayan gwamnan ya dawo daga Masar inda ya tafi kallon wasannin Najeriya.
Buhari ya bayyanawa gwamnan takaicinsa inda ya ce ya sanya hannu a biya ‘y wasan kudadensu amma kuma ba a biya ba, kamar yadda kamfanin dillancin labaran kasar NAN, ya rawaito gwamnan na cewa.
Shugaban ya ce yadda kwallon kafa ke hada kan ‘yan kasa bai kamata a yi wasa da hakkin ‘yan wasan ba.
Ya kuma yi alkawarin daukar mataki kan al’amarin da “gaggawa domin tabbatar da ganin an biya ‘yan wasan kudadensu” domin su kara samun kwarin guiwa a wasanninsu na gaba.
Najeriya dai ta sha kashi hannun Madagascar a wasan karshe na rukuni, bayan Super Eagles sun samu nasara a wasannin da suka buga da Burundi da Guinea.
Sai dai duk da haka ta samu damar kaiwa zagaye na biyu na gasar, kuma a ranar Talata ne za ta san kasar da za ta fafata da ita.