Buhari Na Da Koshin Lafiya – Ndume

VOA Hausa
Shugaban Kwamitin da ke kula da sha’anin dakarun Najeriya a Majalisar Dattawan kasar, Sanata Ali Ndume, ya ce shugaban kasar Muhammadu Buhari na da koshin lafiya.
Ndume, wanda ke wakiltar Borno ta kudu a majalisar, ya yi nuni da irin zirga-zirgar da Buhari ya yi ta yi ba tare da ya nuna gajiyawa ba, yayin ziyarar yini daya da ya kai a jihar Borno.
“Ni kaina na gaji, amma shugaban (Buhari) ya yi ta zirga-zirga har tsawon sa’a shida, tun da ya sauka da misalin karfe 10, mun yi ta zagaya wa har zuwa karfe hudu, kafin daga baya ya tafi.” Ndume ya fada a shirin “Politics Today” na gidan talabijin din Channels a ranar Alhamis
“Saboda haka, duk masu cewa shugaban ba shi da lafiya, magana kawai suke yi, domin sai da muka zagaya yankunan jihar hudu baki daya.”
A cewar Ndume, hakan ya nuna cewa Buhari yana da koshin lafiya, “idan aka duba yadda ya yi hira da Arise TV, ya je Legas, ya kuma zo nan Borno.”
“Ina ga yanzu ya kamata bangaren ‘yan adawa su sake zama su ga me za su yi magana kuma akai,” amma ba batun rashin lafiya ba, a cewar Sanatan.
A ‘yan watannin baya an yi ta raderadin shugaban na Najeriya mai shekara 78 ba shi da koshin lafiya, batun da fadarsa ta musanta.
A karshen watan Maris Buhari ya je London don duba lafiyarsa, inda ya kwashe mako biyu a can.

More News

Ɗalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...