Tawagar kwallon kafa ta Brazil ta bayyana ‘yan wasa 23 da za su buga mata tamaula a gasar Olympic da birnin Tokyo zai karbi bakunci a bana, amma ba Neymar a ciki.
Neymar dan kwallon Paris St Germain, mai shekara 29, baya cikin ‘yan wasa uku da aka amincewa tawaga ta dauki wadanda shekarunsu suka haura 23.
Cikin ukun da za ta je da su Tokyo domin buga mata tamula a Olympic sun hada da Dani Alves da Diego Carlos da kuma Santos.
Brazil wadda ke fatan kare zinare da ta lashe a 2016, bayan doke Jamus, ta zabi Alves ganin cewar yana daga cikin masu sa’a a wasannin tamaula da kan lashewa kungiya ko tawaga kyautuka
Cikin watan Mayu Alves ya cika shekara 38, shima yana fatan kara lashe kyautar lambar yabo a Tokyo domin karawa daga wadanda yake da su tun a baya.
Sauran ‘yan wasa 20 da aka gayyata sun kasance ‘yan kasa da shekara 23, kamar yadda doka ta tanada a gasar kwallon kafa ta Olympic.
Za a fara gasar wasannin Olympic da birnin Tokyo zai karbi bakunci daga ranar Juma’a 23 ga watan Yuli zuwa Lahadi 8 ga watan Agustan 2021.
Tun a bara ya kamata a gudanar da wasannin Olympic, amma tsoron yada cutar korona ya sa aka dage fafatawar zuwa shekarar 2021.
Tawagar Brazil da za ta buga Olympic a Tokyo.
Masu tsaron raga: Santos da kuma Brenno.
Masu tsaron baya: Dani Alves da Gabriel Menino da Guilherme Arana da Gabriel Guimaraes da Nino da kuma Diego Carlos.
Masu buga tsakiya: Douglas Luiz da Bruno Guimaraes da Gerson da Claudinho da Matheus Henrique.
Masu wasan gaba: Matheus Cunha da Malcolm da Antony da Paulinho da kuma Pedro.