‘Biri ya cinye naira miliyan 7 a gidan zoo a Kano’ | BBC Hausa

goggon biri

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Jami’an kula da gidan namun daji na zoo da ke Kano sun ce suna bincike kan wani goggon biri da ya cinye naira miliyan bakwai.

Shugaban gidan zoo din Umar Kashekobo ya ce: “‘Yan sanda na bincike kan ainihin abin da ya fau – abin da zan iya cewa kawai shi ne kudi sun bata.”

Mai magana da yawun ‘yan sandar jihar Abdullahi Kiyawa ya ce kudaden shiga gidan zoo din na kwana biyar ne suka yi batan dabo.

Ya shaida wa BBC cewa zuwa yanzu an kama mutum 10 kuma jami’ai na binciken abin da ya sa ake ajiye kudi mai yawa haka ba tare da kai su banki ba.

A farkon makon nan gidan rediyon Freedom a Kanon ya sanar da bacewar kudin.

Gidan rediyon ya yi hira da wani ma’aikacin bangaren kudi na gidan wanda ya ce goggon birin ya sulale ya shiga cikin ofishin ne ya sace kudaden tare da cinye su.

A shekarar da ta gabata ma wata ma’aikaciya a hukumar shirya jarabawar shiga jami’a ta Jamb reshen jihar Benue, ta ce wani maciji ya shiga ofishin ya hadiye naira miliyan 36 kudin jarabawar da aka tara.

Makonni kadan da suka gabata ita da wasu jami’an suka musanta hannu a batan kudin.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...