Ba Za A Samu Matsalar Karancin Man Fetur Ba – NNPC

Dogayen layuka a gidajen mai na daga cikin alamun da ‘yan Najeriya ke la’akkari da su wajen yiwuwar samun karancin man fetur a kasar.

Kamfanin man fetur na Najeriya NNPC ya ba da tabbacin cewa kasar na da wadataccen mai a ajiye wanda zai iya biyan bukatun daukacin ‘yan Najeriya.

NNPC ya fitar da wannan sanarwa ce a ranar Laraba bayan da layukan mai suka fara kunno kai a Abuja, babban birnin kasar.

Sai dai cikin sanarwar mai dauke da sa hannun Babban Manajan yada labaran kamfanin Garbadeen Muhammad, NNPC ya yi kira ga jama’a da su kwantar da hankulansu.

“Kamfanin NNPC na mai sanar da ku cewa yana da wadataccen mai a ajiye wanda zai biya bukatun ‘yan Najeriya.

“Muna kira ga jama’a da kada su yi ta tururuwar sayen man, su yi watsi da jita-jitar da ke nuna cewa za a samu karancin man.” Garbadeen Muhammad ya ce.

‘Yan Najeriya dai kan yi rige-rigen sayen man fetur su ajiye, a wani mataki na kandagarki, idan sun ga alamu da ke nuna cewa za a samu karancin man.

Dogayen layuka a gidajen mai na daga cikin alamun da ‘yan Najeriya ke la’akkari da su wajen yiwuwar samun karancin man fetur a kasar.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...