An Yi Taro Kan Hanyoyin Sarrafa Kudade A Ma’aikatun Gwamnati

VOA Hausa

AKantocin kudi na jahohi da daraktoci da sauran manyan Jami’an tafiyar da harkokin kudi a ma’aikatu da hukumomin gwamnatin tarayya kana da takwararorinsu na jahohin kasar 36 da kuma birnin tarayya Abuja ne ke halartar taron na yini uku.

Babban akanta janar na tarayya Ahmed Idris, ya fayyace makasudun shirya taron, inda ya ce an shirya taron ne domin tattaunawa akan yadda za’a samar da sababbin hanyoyin da gwamnatocin jahohi da na tarayya za su bi domin samar da kudaden shiga.

Shugaban hukumar EFCC Ibrahim Magu ya ja hankalin mahalarta taron su kiyaye da ka’idojin da doka ta shimfida wajen tafiyar da dukiyar al’umar kasa.

Mataimakin gwamnan Kano Alhaji Nasiru Yusuf Gawuna, wanda ya wakilci gwamna Abdullahi Umar Ganduje, ya ce aiwatarwa tare da sanya ido sosai akan tsarin nan na asusun kudi na bai daya ya bai wa gwamnatin jihar Kano damar like rariyar da kudade ke zirarewa a ma’aikatu da hukumomin gwamnati

Sarkin Kano Malam Muhammadu Sanusi na biyu, ya nanata alakar da ke tsakanin ilimi da habaka tattalin arzikin kowace al’uma, Ya kuma yi kira ga gwamnatoci da su bai wa fannin ilimi kulawar da ta dace.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...