An samu ambaliyar ruwa a Adamawa

Anguwan Tana, al’ummar karamar hukumar Yola ta Arewa, sun shiga tasgaro a ranar Alhamis sakamakon ambaliya daga kogin Kilange da kogin Faro.

Mazaunan garin a babban birnin jihar yana kan gabar kogin Benue, wanda ya ratsa Yola.

Al’ummar sun koka da barnar da suka samu a gonakinsu biyo bayan ambaliyar ruwan.

Da ya ziyarci yankin da lamarin ya shafa a ranar Juma’a, Sakataren zartarwa na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Adamawa, ADSEMA, Dokta Mohammed Suleiman, ya ce da a ce mutane ba su yi kunnen-uwar-shegu da gargadin da aka yi musu ba, da haka bai faru ba.

Shugaban ADSEMA ya shaida wa manema labarai cewa, “Kafin a fara damina, lokacin da muka samu hasashen ambaliyar ruwa, mun gargade su.”

Yayin da yake jaddada bukatar suna bai wa gwamnati hadin kai a kodayaushe, ya ba su tabbacin samar da kayayyakin jin-ƙai.

More from this stream

Recomended