An sace dalibai mata 6 da malamai biyu daga wata makaranta a Kaduna

Akalla dalibai mata 6 da malamai biyu aka sace a kwalejin Engraver dake Kakau Daji a karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna.

Daya daga cikin iyayen daliban da aka sace ya fadawa jaridar The Cable cewa ya amsa kiran waya daga masu garkuwar ranar Alhamis da safe.

“Sun fadawa yata ta basu nambar da za su kirawo shi ne lokacin da suka kirawo ni.Amma kuma na kasa fahimtar ko suna tambayar kudin fansa ne saboda suna magana ne da yaren da bana ji,” ya ce.

“Nayi magana da ‘yata daga nan suka kwace wayar daga hannunta suka katse kiran.”

Yakubu Sabo mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar ya tabbatar da sace daliban inda ya ce yan bindigar sun shiga makarantar ne ta wurin da babu katanga.

Ya ce suna shiga makarantar sun wuce kai tsaye dakin kwanan dalibai mata inda suka sace su.

Ita ma gwamnatin jihar Kaduna ta bakin kwamishinan tsaron cikin gida na jihar,Samuel Aruwan ya tabbatarwa da BBC Hausa faruwar lamarin.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]