An kashe ‘yan Amurka 9 a harin Mexico

Photo of Rhonita Miller and her family

Hakkin mallakar hoto
CBS news

Akalla Amurkawa tara ne suka mutu ciki har da yara shida a wani hari da wasu da ake zargin gungun masu safarar kwayoyi ne suka kai kan wani ayarin motoci a arewacin Mexico.

Wadanda aka kashe na daya daga cikin iyalan gidan LeBaron, wadanda sun dade zaune a Mexico inda suka hada mata uku da yara guda shida.

Ministan tsaron Mexico ya bayyana cewa mai yiwuwa ne wadanda suka kai harin ba wadannan ayarin motocin suka yi niyyar kai wa harin ba, kila akwai wasu na daban da suke dakon su, sai suka far wa ayarin.

Jihar Sinora da ke arewacin Mexico dai na da gungun masu safarar kwayoyi biyu masu rikici da junansu da suka hada da La Línea, wadda take da alaka da gungun Juárez.

Sai kuma abokiyar adawar ta wato Los Chapos wadda tana cikin gungun Sinaloa.

Iyalen wadanda lamarin ya shafa sun tattauna da jaridar New York Times kuma sun shaida cewa cikin yaran biyu da aka kashe basu kai shekra daya da haihuwa ba.

A wani sakon Twitter na Shugaban Amurka Donald Trump, ya bayyana wadanda aka kashe a matsayin abokan arziki wadanda fada tsakanin gungun masu safarar kwayoyi ya rutsa da su.

A cikin jerin sakonnin ya bayyana cewa Amurka a shirye take da ta kai dauki ga kasar.

Shugaban Mexico Andrés Manuel López Obrador, ya bayyana cewa Mexico za ta dauki mataki da kuma kokarin kamo wadanda suka kai harin.

Hakkin mallakar hoto
Reuters

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...